Hausa
Sorah Al-Layl ( The Night ) - Verses Number 21
وَاللَّيْلِ إِذَا يَغْشَىٰ 
( 1 )  
Inã rantsuwa da dare a lõkacin da yake rufẽwa.
وَالنَّهَارِ إِذَا تَجَلَّىٰ 
( 2 )  
Da yini a lõkacin da yake kuranyẽwa.
وَمَا خَلَقَ الذَّكَرَ وَالْأُنثَىٰ 
( 3 )  
Da abin da ya halitta namiji da mace.
إِنَّ سَعْيَكُمْ لَشَتَّىٰ 
( 4 )  
Lãlle ne ayyukanku, dabam-dabam suke.
فَأَمَّا مَنْ أَعْطَىٰ وَاتَّقَىٰ 
( 5 )  
To, amma wanda ya yi kyauta, kuma ya yi taƙawa.
وَصَدَّقَ بِالْحُسْنَىٰ 
( 6 )  
Kuma ya gaskata kalma mai kyãwo.
فَسَنُيَسِّرُهُ لِلْيُسْرَىٰ 
( 7 )  
To, zã Mu sauƙaƙe masa har ya kai ga sauƙi.
وَأَمَّا مَن بَخِلَ وَاسْتَغْنَىٰ 
( 8 )  
Kuma amma wanda ya yi rõwa, kuma ya wadãtu da kansa.
وَكَذَّبَ بِالْحُسْنَىٰ 
( 9 )  
Kuma ya ƙaryatar da kalma mai kyãwo.
فَسَنُيَسِّرُهُ لِلْعُسْرَىٰ 
( 10 )  
To, zã Mu sauƙaƙke masa har ya kai ga tsanani.
وَمَا يُغْنِي عَنْهُ مَالُهُ إِذَا تَرَدَّىٰ 
( 11 )  
Kuma dũkiyarsa ba ta wadãtar masa da kõme ba, a lõkacin da ya gangara (a wuta).
إِنَّ عَلَيْنَا لَلْهُدَىٰ 
( 12 )  
Lãlle aikinMu ne, Mu bayyana shiriya.
وَإِنَّ لَنَا لَلْآخِرَةَ وَالْأُولَىٰ 
( 13 )  
Kuma lalle ne Lãhira da duniya Namu ne.
فَأَنذَرْتُكُمْ نَارًا تَلَظَّىٰ 
( 14 )  
Sabõda haka, Na yi maku gargaɗi da wuta mai babbaka.
لَا يَصْلَاهَا إِلَّا الْأَشْقَى 
( 15 )  
Bãbu mai shigarta sai mafi shaƙãwa.
الَّذِي كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰ 
( 16 )  
Wanda ya ƙaryata, kuma ya jũya bãya.
وَسَيُجَنَّبُهَا الْأَتْقَى 
( 17 )  
Kuma mafi taƙawa zai nisance ta.
الَّذِي يُؤْتِي مَالَهُ يَتَزَكَّىٰ 
( 18 )  
Wanda yake bãyar da dũkiyarsa, alhãli yana tsarkaka.
وَمَا لِأَحَدٍ عِندَهُ مِن نِّعْمَةٍ تُجْزَىٰ 
( 19 )  
Alhãli bãbu wani mai wata ni'ima wurinsa wadda ake nẽman sakamakonta.
إِلَّا ابْتِغَاءَ وَجْهِ رَبِّهِ الْأَعْلَىٰ 
( 20 )  
Fãce dai nẽman yardar Ubangijinsa Mafi ɗaukaka.
وَلَسَوْفَ يَرْضَىٰ 
( 21 )  
To, lalle ne zai yarda (da sakamakon da zã a bã shi).