Noble Quran » Hausa » Sorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent )
Choose the reader
Hausa
Sorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) - Verses Number 44
تَعْرُجُ الْمَلَائِكَةُ وَالرُّوحُ إِلَيْهِ فِي يَوْمٍ كَانَ مِقْدَارُهُ خَمْسِينَ أَلْفَ سَنَةٍ ( 4 )  
 
Malã'iku da Ruhi (Jibrila) sunã tãkãwa zuwa gare Shi, a cikin yini wanda gwargwadonsa, shẽkara dubu hamsin ne.
يُبَصَّرُونَهُمْ ۚ يَوَدُّ الْمُجْرِمُ لَوْ يَفْتَدِي مِنْ عَذَابِ يَوْمِئِذٍ بِبَنِيهِ ( 11 )  
 
Ana sanya su, su gajũna, mai laifi na gũrin dã zai iya yin fansa, daga azãbar rãnar nan, da ɗiyansa,
وَمَن فِي الْأَرْضِ جَمِيعًا ثُمَّ يُنجِيهِ ( 14 )  
 
Da wanda ke a cikin dũniya duka gabã ɗaya, sa'an nan fansar, ta tsĩrar da shi.
تَدْعُو مَنْ أَدْبَرَ وَتَوَلَّىٰ ( 17 )  
 
Tanã kiran wanda ya jũya bãya (daga addini) kuma ya kau da kai.
الَّذِينَ هُمْ عَلَىٰ صَلَاتِهِمْ دَائِمُونَ ( 23 )  
 
Waɗanda suke, a kan sallarsu, su, mãsu dawwama ne.
وَالَّذِينَ فِي أَمْوَالِهِمْ حَقٌّ مَّعْلُومٌ ( 24 )  
 
Kuma waɗanda a cikin dũkiyarsu, akwai wani haƙƙi sananne.
وَالَّذِينَ هُم مِّنْ عَذَابِ رَبِّهِم مُّشْفِقُونَ ( 27 )  
 
Da waɗannan sabõda azãbar Ubangijinsu, suna jin tsõro.
إِنَّ عَذَابَ رَبِّهِمْ غَيْرُ مَأْمُونٍ ( 28 )  
 
Lalle ne, azãbar Ubangijinsu bã wadda ake iya amincẽwaba ce.
إِلَّا عَلَىٰ أَزْوَاجِهِمْ أَوْ مَا مَلَكَتْ أَيْمَانُهُمْ فَإِنَّهُمْ غَيْرُ مَلُومِينَ ( 30 )  
 
Sai fa a kan matan aurensu da abin da hannayensu na dãma suka mallaka. To lalle ne sũkam ba waɗanda ake zargi ba ne.
فَمَنِ ابْتَغَىٰ وَرَاءَ ذَٰلِكَ فَأُولَٰئِكَ هُمُ الْعَادُونَ ( 31 )  
 
To, duk wanda ya nẽmi abin da yake a bayan wannan, to, waɗancan sũ ne mãsu ƙetare iyãka.
وَالَّذِينَ هُمْ لِأَمَانَاتِهِمْ وَعَهْدِهِمْ رَاعُونَ ( 32 )  
 
Kuma da waɗannan da suke ga amãnõninsu da alkawarinsu mãsu tsarẽwa ne.
وَالَّذِينَ هُم بِشَهَادَاتِهِمْ قَائِمُونَ ( 33 )  
 
Kuma da waɗanda suke, ga shaidarsu, mãsu dãgẽwa ne.
وَالَّذِينَ هُمْ عَلَىٰ صَلَاتِهِمْ يُحَافِظُونَ ( 34 )  
 
Kuma waɗanda suke, a kan sallarsu, mãsu tsarẽwa ne.
أُولَٰئِكَ فِي جَنَّاتٍ مُّكْرَمُونَ ( 35 )  
 
Waɗannan, a cikin gidãjen Aljanna, waɗanda ake girmamãwa ne
فَمَالِ الَّذِينَ كَفَرُوا قِبَلَكَ مُهْطِعِينَ ( 36 )  
 
Mẽ yã sãmi waɗanda suka kãfirta, a wajenka, sunã gaugãwar (gudu).
عَنِ الْيَمِينِ وَعَنِ الشِّمَالِ عِزِينَ ( 37 )  
 
Daga jihar dãma, kuma daga jihar hagu, jama'a-jama'a!
أَيَطْمَعُ كُلُّ امْرِئٍ مِّنْهُمْ أَن يُدْخَلَ جَنَّةَ نَعِيمٍ ( 38 )  
 
Shin kõwane mutum daga cikinsu yana nẽman a shigar da shi a Aljannar ni'ima ne (ba da wani aiki ba)?
كَلَّا ۖ إِنَّا خَلَقْنَاهُم مِّمَّا يَعْلَمُونَ ( 39 )  
 
A'aha! Lalle Mũ, Mun halitta su, daga abin da suka sani.
فَلَا أُقْسِمُ بِرَبِّ الْمَشَارِقِ وَالْمَغَارِبِ إِنَّا لَقَادِرُونَ ( 40 )  
 
Sabõda haka ba sai Na yi rantsuwa da Ubangijin wurãren ɓullõwar rãna da wurãren fãɗuwarta ba, lalle Mũ, Mãsu iyãwa ne.
عَلَىٰ أَن نُّبَدِّلَ خَيْرًا مِّنْهُمْ وَمَا نَحْنُ بِمَسْبُوقِينَ ( 41 )  
 
Ga Mu musanya waɗanda suke mafi alhẽri, daga gare su. Kuma ba Mu kasance waɗanda ake rinjãya ba.
فَذَرْهُمْ يَخُوضُوا وَيَلْعَبُوا حَتَّىٰ يُلَاقُوا يَوْمَهُمُ الَّذِي يُوعَدُونَ ( 42 )  
 
Sabõda haka ka bar su, su dulmuya, kuma su yi wãsã, har su haɗu da rãnarsu wadda ake yi musu alkawari (da ita).
Random Books
- Matsayin Mata A Musulunci, Yahudanci da Nasaranci-Source : http://www.islamhouse.com/p/191549 
- QADDARA TA RIGA FATA-Source : http://www.islamhouse.com/p/156356 
- KYAKKYAWAR SAFIYA-Source : http://www.islamhouse.com/p/156350 
- Rayuwar Annabi Sallallahu Alaihi Wasallama A Lokacin Aikin Hajji-Source : http://www.islamhouse.com/p/156193 
- TAFARKIN SUNNAHTAFARKIN SUNNAH tattaunawa ta ruwan sanyi tsakanin ibnu taimiyyah da ‘yan shi’ar zamaninsaSource : http://www.islamhouse.com/p/172222 















